Skip to main content

Kowa yayi da kyau



NASIHA DAGA HUKUMAR A DAIDAITA SAHU, KANO STATE

(BANGAREN RASHIN DA'AR MA'AIKATA)



Na

SADISU MUSA MANDAWARI



1

"Aminu da Usman abokan juna ne, tare suka tashi, tare sukai karatu, Aminu Turanci ya kaanta a jami'ar Bayero ta Kano, shi ko Usman ya karanta lissafi ne a jami'ar Oxford ta Ingila, tare suka fara amma Usman ya riga Aminu gamawa saboda wahalar karatu a Najeriya, sannan wasu matsaloli sukan tasowa jami'o'in Najeriya a kullesu.

A yanzu dai sun gama karatu, kuma sun sami sakamako irin wanda duk wani dalibi ya ke so ya samu malamai da abokan Usman suna matukar kaunarsa, saboda da'arsa, da kuma hakurinsa.

Abokan Aminu da Usman, sun haxu sun shirya musu walimar gama karatu lafiya da samun sakamako mai kyau.

Karamci da zumunci da 'yan uwanta da Aminu da Usman su ka gani ja wurin abokansu shi ne ya sasu zubar da hawaye, wanda a lokacin da aka nemi su yi jawabin godiya, hakan ta qi samuwa saboda a lokacin ne hawaye ke zuba daga idanunsu, na farin ciki.

Malam Bako kwararre ne a harkar koyarwa shi ne aka roka ya yi jawabi a matsayinsu, a karshe aka yi addu'a aka baje.

Bayan sati daya, Aminu ya zo wurin abokinsa Usman, don su yi shawara su ga wanne aiki ya dace su nema, bayan sun gama gaisawa shi kuma Aminu ya huta sai ya ce "Usman na zo ne mu yi shawara, mu ga wanne aiki ya dace mu nema?" Sai Usman ya ce "Aminu ni fa na tsorata da aiki a karqashin gwamnati, sai Aminu ya ce haba Usman in ba mu yi wa gwamnatin jahar mu aiki ba to ai mun ci amanar ta, domin da kudin wannan jiha tamu mu kai karatu tun daga firamare har zuwa jami'a gaskiya ne Aminu, Usman ya fada to wai me ya tsorata ka ne Usman da ba ka so ka yi aiki a gwamnatin jihar ka?" Aminu ya tambaye shi cikin mamaki.

Usman ya yi shiru na dan wani lokaci,sannan ya daga kai ya kalli Aminu ya ce "Aminu rashin da'a da rashin ganin girman na gaba, a cikin gwamnati uwa uba bayyana sirrin gwamnati da ya yi katutu a zukatan ma'aikata a yau, ina so ka sani, Aminu babu wata ma'aiakta da take karkashin gwamnati a yau da ma'aikatanta suke da cikakkiyar da'a da boye sirrin wannan ma'aikata. Cikin nutsuwa, da sanyin murya, Usman ya ce "Aminu yau ta kai hatta gidan gwamnati ba shi da sirri saboda rashin xa'ar ma'aikata, Aminu ya ce ni abin da nake so Usman shi ne ba ka bani misalan irin rashin da'ar ma'aikatan sunann ka bayyana mini wanne irin sirri ne suke bayyanawa? Ta haka zan gamsu cewa gaskiya ka ke faxa mini don  kaima kada ka rufta cikin 'yan jita-jita, kuma ina so ka sani Usman kai fa ka na da na'urar dake yi ma saiti, to ka gama?" Usman ya tambayi Aminu, na zo mdai aya Aminu ya faxa, to ina so ka saurara ka ji irin rashin xa'ar ma'aikatan wannan jiha tamu mai albarka, da kuma irin yadda suke bi suka bayyana sirrin gwamnati ka ga dai da farko ma'aiakatan gwamnati irin su:-

1. Ma'aikatar ilimi

2. Ma'aikatar tsara birane

3. Ma'aikatar gona

4. Ma'aikatar lafiya

5. Ma'aikatar ayyuka da gidaje

6. Ma'aikatar watsa labarai

7. Ma'aikatar qananan hukumomi

8. Ma'aikatar harkokin mata

9. Ma'aikatar ruwa

Wadannan kasan ne daga cikin ma'aikatan da suke qarqashin gwamnatin jiha amma rashin da'a da bayyana sirrin waxannan ma'aikata ya yi katutu a zukatan ma'aikatan, bari in dau uku daga ciki in kawo irin rashin xa'arsu da bayyana sirruns wanda bai dace su yi haka ba.



MA'AIKATAR ILIMI



Yau in kwamishina ya yi mitin da sakataren sa, ko daraktocin sa, kafin shugabannin makarantu su ji, mutanen gari sun ji kana shugaban makaranta amma sai ka ji wani zauna gari banza yana baka labarin abin da zai faru a makarantar ka gobe.

Wani lokaci kuma malamai sune suke zuwar wa da shugabannin makarantar abubuwan da ma'aikatar ilimi take tsarawa makarantu.

Kai wani lokaci malami za a tura wata makaranta amma sai shugaban makarantar bai sani ba, haka kuma za a daukeshi bai sani ba.



MA'AIKATAR KANANAN HUKUMOMI



Sau da yawa za a tsara wani abu da za a yi a wata qaramar hukuma a wani kauye, amma kafin bayanin ya je wurin shugaban wannan karamar hukuma daga jaha tuni labarin ya je wurin mutanen wannan karamar hukuma sai daga baya bayani a rubuce ya isa karamar hukuma.



MA'AIKATAR GIDAN GWAMNATI



Yau duk wani abu da gwamna zai tsara in dai ya fito da shi daga zuciyarsa wasu su ka ji cikin wata daya zuwa biyar wasu sun watsa labarin cikin gari, wadanda ya dace su ji a tsarin gwamnati sai dai daga baya su ji ko takarda ta iso wurinsu bayan abu ya zama tsohon ya yi.

Usman ya ci gaba da cewa Aminu sirrin gwamnati yana fita ne ta hanyar matan ma'aikata, ko kuma ta hanyar sakatarorin gwamnati ko kuma ta hanyar yaran ma'aikata ga misali;



In aka yi mitin da wani darakta da ya zo gida in hira ta yi dadi da matarsa sai ya hau zubar mitin din da aka yi da shi, ita kuma da ta kwashe sai ta bayyanawa wata kawar ta shirye-shiryen gwamnati.

Wani lokaci kuma sakatarori ne da an aiko da wani bayani daga gidan gwamnati zuwa ma'aikatarsu da ya gani sai kwafi na takardar ya saye ya fita da ita don kawai a ce ya burge su ne gwamnati.

Wani lokaci zumudin wani shugaba ne da an yi mitin da shi in ya dawo gdia sai ya kirawo wanda akai mitin din a kan su, ya ce.

"Kai wannan maganar mun gama da ita jiya kuma kana ciki, in kuma wani abu ne sai ya ce dashi ka je ba wani abu da ya faru, to daga nan fa shi wnanan zai shiga kwaza maganar, kusan wadannan su ne hanyoyi da sirrin gwamanti ya ke fita.

Amma batun rashin da'ar ma'aikata a wannan fili yake ba sai na tsaya yi maka wani dogon bayani ba.

Yau lebura zai iya sharrin da ya ga dama ga shugabansa, shi kuma shugaba zai iya zubarwa da kansa mutunci a gaban ma'aiaktansa bai damu ba saboda yana ganin shi ne shugaba,

Bayan duk Usman ya gama dogon bayaninsa sai Aminu ya ce to Usman ni kuma sai ka saurareni don ka ji nawa batun.

"Ka sani Usman bamu da wata jaha da tafi wannan jaha tamu idan har muka tsame hannunmu to waye zai zo ya gyara mana?" Bayan mu ne 'yan gidan kuma mune muka san maganin wannan cuta saboda da haka shiga za mu yi har Allah ya kai mu ga teburin da ya ke da qarfin ikon hana wasu mugayen ayyuka ga ma'aikatan gwamnati.

Ina so ka sani Malam Usman wanke zuciyar mu za mu yi, mu tsaya tsayin daka mu ga mun daidaita sahun ma'aikatan wannan jaa ta mu.

Bayan Aminu ya wayar da kan Usman abokinsa, sai ya yarda ya amince zai nemi aiki a gwamnatin jahar sa.

Bayan kwana biyu suka rubuta wasikun neman aiki inda cikin wata daya aka dauke su.

Kowa ya sami aiki a inda ya dace dashi saboda shi Aminu da ya karanta Turanci an kai shi KERD bangaren kula da da jarabawar Turanci a matsayin sakataren darakta, shi kuma Usman bangaren akawun na jiha a matsayin mai binciken kudi na jaha.

Cikin kanqanin lokaci 'yan bani na iya, 'yan tumasanci, 'yan hana ruwa gudu su kai ca zuwa ofishin su.

Da mutane suka ga sun zo da kwakkwarar niyya sai surutai sai sharri suka fara tasowa, wasu suna cewa sa yi sa gama, wasu suna cewa anyi wadanda suka fi su amma yau suna ina duk wadannan batutuwa da suke faruwa suna ji amma sai suka yi shiru don su cimma burinsu.



2

Bayan shekara goma sha biyu da fara aikinsu a ma'aikatun gwamnati sai da'ar su da kwazan su da dagewar su kan gaskiya ta futo a fili sannan sai ya zama duk wani gwamna da ya zo sai ya tafi da su.

"A kwana a tashi sai daya daga cikin su ya kama rashin lafiya kamar ya mutu shi ne Usman saboda shine yafi shiga matsala kasan cewar ya zama babban mai binciken kudi na jiha amma Allah cikin rahamar sa ya bashi sauki kuma yawar ke sarai kamar baiyi ba.

Kimanin kwana uku kenan ana bayyana cewa gwamna zai yi sauye sauye a gwamnatin sa gaba daya saboda yaga mafi yawan ma'aikatun jihar masu aiki a wurin ba su da da'a sannan sirrin gwamnati yaki buya musamman gidan gwamnatin kanta.



Kafin gwamna ya yi jawabi sai da ya shawarci na kusa da shi a kan yana so a bashi sunayan mutane masu da'a da kwazon aiki, a cikin mutum goma da gwamna ya nema su lalubo masa mutane masu kwazo mutum shida sunan, Aminu su ka bayar mutum uku kuma suka ba da sunan Usman mutum daya kuma shi ne ya ba da sunan wani dan jarida.

"Yau ita ce rana da mafi yawan ma'aikata su ka kasance a gidajansu saboda suna saurarar lokacin da gwamna  zayi jawabi da misalin 5:30 zuwa 6:00 P.M.

" lokaci na cika gwamna ya fara da sunan Allah da yabo da Annabi Muhammad (S.A.W) sannan ya yabawa kwazon wasu ma'aikatu ya kuma zargi wasu a karshe ya bar wasu ba yabo ba suka.

"Kai tsaye gwamna ya ya bawa mutanen gari, da wasu mutane masu san kawo zaman lafiya a jiha sannan ya ciga ba da cewa na san yau kusan wata shida al'ummar wannan jiha tamu mai albarka su ke sauraran suji jawabina amma shiru sai yau Allah ya nufa.

"Bayan gwamna ya gama jawabin sa sai ya ba da sanarwar cire kwamishinoni har guda (5) tare da sakataran sa, sai gari ya dau sowa wasu suna godewa gwamna saboda suna ganin yan zu gyara zai zo, amma wasu tsiraren mutane yan hana ruwa gudu suna ganin gwamna ya yi bambarama, ya kashe kansa domin wadanda ya cire su ne shi ba zai iya komai ba sai da su.

Gwamna yaci gaba da cewa ya nada Aminu a matsayi sakataren gwamnati sannan ya yi sallama aka saka taken qasa.

Bayan wata daya da rantsar da sababbin kwamishinoni da sakataren gwamnati sai aiki ya kankama kowa ya shiga taitayin sa.

Tsari farko da Aminu ya fara aiwatarwa shi ne mitin da daraktoci ya bayyana musu cewa za a basu miliyan 20 a kowacce ma'aikatar su dan su yi gyare-gyare.

Cikin kwana daya sai ya ji magana ta watsu a ma'aikatu da cikin al'umma, cikin gaggawa ya tara wadanda ya yi mitin da su ya tambayesu yaya haka ta faru? Shiru ba amsa, amma a satin aka sauya musu ma'aikata sannan aka hada musu da takardar jan kunne.

Haka sakataren gwamnati Aminu ya ringa aiwatar wa daya bayan daya ba tsoro ba ja da baya bisa yardar gwamna sai gashi sama da rabin ma'aikatu sun gyara.

Akwai wata matsala da taki ci ta ki cinye wa a ma'aikatun gwamnati ita ce ta boye fayel din ma'aikata amma cikin sauki aka sami warwarewar al'amura cikin sauki.

Bayan komai ya sami daidaita a harkokin gwamnati sai gwamna ya tara kwamishinoninsa ya bayyana musu cewa, ya zama wajibi kowa ya ji tsoron Allah ya sani duk wata nasara da su ke samu ta na samuwa ne sakamakon tsarkake zuciya da ma'aikata suke yi ahalin yanzu.

Daga nan sai mai girma gwamna ya ce yanzu kasancewar da'a da sirrin gwamnati sun sami gindin zama a halin yanzu to ya zama wajibi a baiwa ma'aikata duk wani hakkinsu.

Cikin shekara daya da watanni ya zama wannan jiha ta zama abar koyi ga sauran jihohin kasar.

Karfe 8 na safe kowanne ma'akaci na wannan jiha ya isa wurin aikinsa saboda shima yana samun abin da ya dace a msatainsu na ma'aikaci.

Alhamdulillahi

Sadisu Musa Mandawari.

Comments

Popular posts from this blog

25 Years After Abubakar Imam: Where are the Inheritors?

Dr Ibrahim Malumfashi, July 1, 2006 This year, specifically this month of June marks the 25th year of the demise of Abubakar Imam, the foremost Northern writer and journalist. On the occasion of this anniversary, I wish to use this medium to highlight the comatose nature of Hausa written literature since that time and have a look at the inheritors of Imam and his age that permeates the Northern literary landscape. In doing that we hope to be able to lay things bare as far as the development of the literature is concerned. I think there is the need for this kind of soul searching from time to time so that we can come to terms with the reality of our times and construct a future without hiccups for our nascent literature. I will begin this discourse by repeating the well-known axiom I have been articulating for the last 15 years. I have this belief that in the North and among any age group of writers that once existed or still exist, there was none like Imam, none like him today a

Begin with a smile or laughter

By Habu Dawaki Some of the best sets of people that teach us about life are children. Among other things, children are known for their innocence, simplicity, purity of heart, frankness, spirit of forgiveness, genuineness, receptivity, trust, dependence, curiosity, energy, enthusiasm, of, wonder, open-mindedness and teachability. Children seem to know how to love and enjoy life rather than endure it. They appear to always have time to still play, sing, smile and laugh. A closer look at children reveals that they have no stress, high blood pressure and so on. I believe this is partly because they worry less. If they ever have problems at all, they simply hand them over to someone bigger than them. This could be their parents, guardians, teachers, aunts, or uncles, just to mention a few. I think children have an understanding that carrying all our burdens alone is destructive and injurious to our physical, mental, emotional and spiritual well-being. It is said that the average chil

Corruption And Other Matters

By Wada Nas, September 4, 2004 Since the death of General Sani Abacha, I cannot recall a day when reference is not made to his so-called loot in the media. It has been a daily affair even when we all agree that the issue of corruption is worse today than it has ever been. For General Obasanjo in particular, it has been one of his sing-songs and prayer verse. His government has given the impression that Abacha is the only corrupt persons who ever lived in Nigeria, while he Obasanjo and his government are the most decent and clean saints we ever had or will ever have. Of course Nigerians know the truth about the state of corruption in Nigeria today. We do not need to recall the past about missing N350 billion annually from NNPC accounts whose senior minister is the general. Nor do we need to mention how he blocked the Na’ Abba led House of Representatives from looking into the books of the corporation. Reports about corruption have been occurring daily in the papers, enough such